38.4 C
Kano
Wednesday, March 11, 2026

Dole ne a bincika zargin lalata tsakanin Sanata Natasha da Akpabio – Amnesty

Ƙungiyar kare haƙƙi ta duniya Amnesty International ta ce ya zama wajibi a bincika zarge-zargen da Sanata Natasha Akpoti ta yi wa Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Godswill Akpabio na neman yin lalata.

Jam’iyyar adawa ta PDP a Najeriya ta zargi shugaban majalisar da tauye wa sanatan haƙƙin wakiltar jama’ar mazaɓarta na jihar Kogi sakamakon matakin majalisa na dakatar da ita tsawon wata shida kan rashin ɗa’a ga majalisa.

Cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar a Najeriya ya fitar, Isa Sanusi ya ce: “Amnesty na kira ga mahukuntan Najeriya da su fara gudanar da sahihin bincike cikin gaggawa game da zargin lalata da Natasha ta yi wa Akpabio.

“Girman zargin ɗaya ne daga cikin dalilan da za su sa a gudanar da bincike mai zaman kansa kuma sahihi.

“Idan hukumomin Najeriya suka gaza bincika wannan zargi zai jawo matsala mai girma, ciki har da kawo tsarin da zai dinga hana waɗanda aka ci zarafi ta hanyar lalata samun adalci.”

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa