39.6 C
Kano
Tuesday, April 14, 2026

Kungiyar NLC Ta Yi Barazanar Zanga-Zanga Kan Hana Sanata Natasha Komawa Majalisa

Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta gargadi majalisar dokoki cewa za ta fito da mambobinta yin zanga-zanga idan aka ci gaba da hana Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, komawa bakin aiki bayan dakatarwar da aka kammala.

Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya fitar da sanarwar ne a ranar Alhamis, inda ya bayyana cewa ci gaba da tsare mata hanya ya saba wa tsarin dimokuradiyya, yana mai cewa abin da ya faru da dan majalisa guda na iya zama hari kan ’yan Najeriya baki daya.

Sai dai har yanzu ba a bayyana ko NLC za ta fito da gaggawa yin zanga-zanga idan aka cigaba da hana sanatar dawowa aiki ba, musamman ganin an rage jiran hukuncin kotu kan dakatarwar.

A farkon makon nan kuwa, lauyar Sanata Natasha ya yi barazanar kai kara gaban kotu idan aka hana ta komawa bakin aiki kafin Litinin mai zuwa.

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa