35.1 C
Kano
Monday, May 19, 2025

Dambarwa ta kaure a majlisar dattawan Najeriya

Hayaniya ta kaure a zauren Majalisar Dattijan kasar Najeria yayin da sanatoci ke muhawara kan zargin cushe a cikin kasafin kuɗin ƙasar, wanda shugaban ƙungiyar sanatocin arewa, Abdul Ningi ya yi a wata tattaunawa da sashen Hausa na BBC.

Tun da farko shugaban kwamitin kasafin kuɗi na majalisar Sen. Olamilekan Adeola daga jihar Ogun ya gabatar da ƙorafi kan tattaunawar da Sanata Ningi ya yi da sashen Hausa na BBC.

Ya soki lamirin kalaman Sanata Ningi kan cewa ana amfani da kasafin kuɗi iri biyu a ƙasar.

Sanata Adeola ya ce wannan tamkar cin zarafi ne da kuma ƙazafi.

Ya bayyana cewa kalaman sanata Ningi ba gaskiya ba ne, kasancewar tun asali babu kuɗin da aka ware a wasu ma’aikatu a cikin kasafin kuɗin da majalisar ta amince da shi.

Sai dai Sanata Adamu Aliero daga jihar Kebbi ya bukaci shugaban majalisar dattijai, Godswill Akpabio ya yi adalci wajen jin tabakin Sanata Ningi kan kalamansa a hirarsa da BBC Hausa.

A lokacin da ya yi sa’ilin muhawarar, Sanata Abdul Ningi ya bayyana cewa an yi wa kalaman nasa mummunar fassara ce

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa