22.6 C
Kano
Tuesday, January 13, 2026

Tinubu y ba da umarnin sake Karya farashin kayan Abinci a Nigeria

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bai wa wani kwamiti na majalisar zartarwar ta tarayya umarnin daukar karin matakai don rage farashin kayan abinci a fadin kasar nan.

Minista a Ma’aikatar Noma, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi, ne ya bayyana haka an Abuja ranar Laraba.

Sanata Abdullahi ya bayyana cewa za a aiwatar da wannan umarni ta hanyar tabbatar da tsaro domin wucewa da kayayyakin amfanin gona da sauran kayan abinci cikin kwanciyar hankali a kan manyan hanyoyi a duk fadin Najeriya

Ya kara da cewa wannan mataki na daga cikin hangen nesa na shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu wajen cimma manufar sauko da kayan abinci mai dorewa a kasar.

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa