33 C
Kano
Saturday, September 6, 2025

Jam’iyyar APC ta bayyana matsayarta kan zaben cike gurbi a Kano

Jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe ta dakatar tare da soke zaɓen cike gurbi da ke gudana yanzu haka a jihar Kano saboda “tashin hankali”.

Wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar ta ce ‘”‘yandaba sun tarwatsa kayayyakin zaɓe a ƙananan hukumomin Bagwai da Shanono da Gari”, inda ake gudanar da zaɓen ɗanmajalisar tarayya.

A cewarta: “Cigaba da kaɗa ƙuri’a a irin wannan yanayin na dabanci da tilasta wa masu zaɓe ya saɓa da tanadin dimokuraɗiyya na gudanar da sahihin zaɓe, kuma zai koyar da satar ƙuri’a da ba za a yarda da shi ba,” in ji sanarwar.

Duk da cewa APC ce riƙe da mulkin a tarayya, NNPP ce mai mulki a jihar ta Kano da ke arewacin ƙasar.

Zuwa yanzu ba a kai ga samun sakamakon zaɓen a hukumance ba, yayin da ake ci gaba da kaɗa ƙuri’a a wasu rumfunan zaɓe

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa