34.4 C
Kano
Sunday, September 7, 2025

Ambaliya ta kashe sama da mutum 20 a jihar Neja

Hukumomi a jihar Neja da ke arewacin Najeriya sun tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 21 sanadiyyar wata mummunar ambaliyar ruwa a ƙaramar hukumar Mokwa.

Haka nan sun ce ya zuwa yanzu akwai aƙalla mutum 10 da ba a san inda suke ba.

Shugaban hukumar bayar a agajin gaggawa ta jihar, Ibrahim Hussaini ya ce lamarin ya kuma lalata aƙalla gidaje 50 a ƙauyukan Tiffin Maza da Anguwan Hausawa na ƙaramar hukumar Mokwa, bayan shafe sa’oi ana zabga ruwan sama mai ƙarfi.

Yanzu haka masu aikin ceto na ci gaba da aikin neman mutanen da ambaliyar ta rutsa da su.

Wani da abin ya faru a idonsa ya ce ruwa ya mamaye unguwannin a cikin dare bayan mamakon ruwan da aka shatata

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa