22.6 C
Kano
Tuesday, January 13, 2026

Dalilin da yasa bana fargabar mutuwa:Remi Tinibu

Mai dakin Shugaban kasa Bola Ahmed Tinibu tace yanzu haka shekarunta na haihuwa sun kai 60 don haka tayi tsufa da bata fargabar mutuwa

jaridar Aminiya ta ruwaito Remi Tinubu ta bayyana hakan ne a Fadar Sarkin Bauchi, Dokta Rilwani Suleiman Adamu ranar Talata, kan wani bidiyon barazanar kisa da wani malami Sunusi Abubakar ya yi mata a kwanakin baya.

Remi ta kai ziyara jihar ne domin kaddamar da aikin makaranta da cibiyar horaswa kan fasahar bayanai da gwamnati ta yi a jihar.

A kwanakin baya ne dai bidiyon ya karade soshiyal midiya, inda malamin ya ce ya kamata a kawar da ita daga doron kasa, kafin daga bisani ya janye kalamansa bayan shan suka daga mutane.

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa