22.9 C
Kano
Monday, January 19, 2026

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun hutun karamar Sallah

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Sallah Ƙarama

Ministan Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da Magdalene Ajani, Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, ta fitar a ranar Laraba.

Ministan ya taya daukacin al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da yin kira ga al’ummar 3su rungumi dabi’un hakuri, tausayi, kyauta, da zaman lafiya.

Ya kuma bukaci ‘yan Najeriya su yi amfani da wannan dama wajen yin addu’o’i don zaman lafiya, daidaito, da ci gaban kasa.

Tunji-Ojo ya yi fatan cewa wannan biki na Sallah Ƙarama zai kara hadin kai da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai da kabilu daban-daban a kasar.

A karshe, ya bukaci jama’a da su yi bukukuwa cikin lumana da kiyaye doka, tare da tunawa da marasa galihu ta hanyar ayyukan alheri .

Gwamnati ta kuma aika da fatan alheri na Eid Mubarak ga daukacin al’ummar Musulmi, tana mai addu’ar Allah Ya kawo albarka, nasara.

 

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa