28.6 C
Kano
Friday, April 25, 2025

Zanga-zanga Ta Barke a Jos Sakamakon Kashe-kashe Na Harin ‘Yan Bindiga

Wasu mazauna garin Jos, babban birnin jihar Filato, sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da sace-sacen mutane da kashe-kashe da ‘yan bindiga ke yi a jihar.

Ayarin mutanen karkashin jagorancin shuwagabannin kiristoci da suka hada da shugaban kungiyar kiristoci ta jihar, Rev. Polycarp Lubo, ta faro ne a safiyar yau litinin, wanda ya haifar da cunkoson ababen hawa.

Zanga-zangar ta baya-bayan nan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun munanan hare-hare da ‘yan bindiga ke kai wa a al’ummomi daban-daban, inda aka kashe sama da mutane 100 a karamar hukumar Bokkos da Bassa cikin makonni biyu da suka gabata.

A halin yanzu dai ana ci gaba da gudanar da jerin gwano na yaki da hare-hare da kashe-kashen da wasu ‘yan bindiga suka yi wa al’umma a kauyuka da yankunan jihar Filato a Jos babban birnin jihar, bisa jagorancin kungiyar Kiristoci.

Labarai masu alak'a

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Kasance tare da mu

0FansLike
0FollowersFollow
0SubscribersSubscribe

Sababbin Wallafa